2023: Daruruwan jama'a sun gudanar da gangamin fadakarwa na shirin yakin neman zaben Rotimi Amaechi a jihar Kebbi.


Daruruwan magoya bayan Rotimi Amaechi a karkashin Amaech Vanguard a jihar Kebbi, a ranar Asabar 23 ga watan Afrilu, 2022, sun gudanar da wani gangamin nuna goyon baya a Birnin kebbi suna rera taken goyon baya da kuma nuna alluna dauke da rubuce-rubucen hadin kai domin nuna goyon baya ga Mista Ameachi.

Tsarin da ya sami goyon bayan da ba zato ba tsammani daga sauran jama'a yayin da mutane suka shiga jerin gwano bisa radin kansu suka Kara armashi ga tsarin wanda ya sami gagarumar nasara.

Shugaban kungiyar  na jihar Kebbi kuma kodinetan Amaech Vanguard a jihar Kebbi, Kwamared Shamsu Muhktar ya shaidawa manema labarai cewa:


"Tsarin dai ya faro tun daga matakin kasa har zuwa jihar Kebbi . Mun yanke shawarar shirya wannan gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na Rotimi Amaechi domin mu tallata shi ga al’ummar jihar Kebbi.

Mun yi imanin cewa akwai wani dan jihar Kebbi da ke rike da matsayi mai mahimmanci a ma'aikatar sufuri mai suna Mande Koko, shi ne Manajan Daraktan Hukumar Tashoshin Ruwa ta Najeriya. Don haka ne mu al’ummar jihar Kebbi muke tunanin idan akwai jihar da za ta goyi bayan Ameachi baya ga jihar Ribas jihar Kebbi ta zama ta biyu.


Don haka ne a yau muka taru tare da jama’armu manya da yara maza da mata don nuna goyon bayanmu, dalilin shi ne wannan mutumi yana hade Nijeriya. Ya kasance Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Ribas daga 1999 zuwa 2007 kuma   a lokacin ya kafa Speakers Forum of Nigeria ya zama shugaba, sannan lokacin da ya zama Gwamnan Jihar Ribas ma ya yi irin wannan abu.

Ya kafa kungiyar gwamnoni sannan ya zama shugaban kungiyar na farko. Ya kuma kasance babban daraktan yakin neman zaben Muhammadu Buhari a zaben shugaban kasa na 2015 wanda Buhari ya lashe zaben. A karkashin ma’aikatar sufuri, mun ga irin namijin kokarin da ya yi, ya hada Nijeriya da hanyar dogo a kowane lungu da sako na kasar nan.


Daga Ibadan zuwa Legas, Abuja zuwa Kaduna, Maiduguri zuwa Fatakwal, titin jirgin kasa daga  Katsina zuwa Maradi, Amaechi ya sake farfado da su a matsayin ministan sufuri, domin kuwa fannin ya dawwama cikin durkushewa kusan shekaru arba’in, amma albarkacin jagorancinsa da manufarsa aka farfado da su. Don haka ne muke kira ga al’ummar jihar Kebbi da ‘yan Nijeriya masu jin mu cewa mu ba shi cikakken goyon baya".

Mu wadanda suka shirya wannan gangamin, ba ma yada tashin hankali ba, muna ba da gudummawa ga kokarin gwamnatin jihar wajen ganin jihar Kebbi ta samu zaman lafiya fiye da sauran sassan kasar nan.






Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN