Yanzu yanzu: Kotu ta tasa keyar Abba Kyari zuwa magarkama, duba yadda ta faru..


Wata babbar Kotun tarayya mai zamanta a Abuja ta tasa keyar Abba Kyari da wasu abokan harkallarsa su shida zuwa magarkamar NDLEA har zuwa ranar 14 ga watan Maris 2022.

Biyo bayan gurfanar da Kyari da abokan harkallarsa, da cacan kaki na shari'a da ya gudana tsakanin Lauyoyin Kyari da na hukumar NDLEA a cikin Kotu, Alkalin kotun Justice Emeka Nwite ya umarci a kai Kyari tare da abokan harkallarsa zuwa magarkamar NDLEA har zuw ranar 14 ga watan Maris.

Abokan harkallar Kyari da suka gurfana a Kotu sun hada da  Mataimakin Kwamishinan yansanda ACP Sunday Ubua, Mataimakin Superintendent na yansanda ASP Bawa James, Inspector Simon Agirigba, Inspector John Nuhu, Chibuinna Patrick Umeibe da Emeka Alphonsus Ezenwanne.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN