Abokan harkallar Abba Kyari 2 sun amsa laifin da ake tuhumarsu dashi
Bayan kawo Abba Kyari da abokan harkallarsa shida gaban kotu da safiyar yau Litinin, an bijiro da tuhume-tuhume da ake yi musu, sai dai, Abba Kyari da wasu mutum hudu da ake zargi sun musanta zargin da ake musu.
A gefe guda, wasu biyu daga ciki sun amsa laifinsu, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito cewa:
"Yayin da Kyari, sanye da shudin riga, da ‘yan sandan da ake tuhuma tare dashi, suka ki amsa laifin da ake tuhumar su da shi, wadanda ake tuhuma na 6 da na 7, Umeibe da Ezenwanne, sun amsa laifin da aka karanta musu a gaban kotun mai shari’a Emeka Nwite."
Da yake tabbatar da laifin da ya aikata, Umeibe ya kuma roki mai shari'a da ya tausaya masa, inji jaridar The Nation.
Legit
Rubuta ra ayin ka