Hotunan yadda aka gurfanar da Abba Kyari a gaban Kotu, abin da ya faru a zaman ..

Abokan harkallar Abba Kyari 2 sun amsa laifin da ake tuhumarsu dashi


A yau ne aka gurfanar da Abba Kyari da mutum shida da ake zarginsu a wata harkallar miyagun kwayoyi ta kasa da kasa.

Bayan kawo Abba Kyari da abokan harkallarsa shida gaban kotu da safiyar yau Litinin, an bijiro da tuhume-tuhume da ake yi musu, sai dai, Abba Kyari da wasu mutum hudu da ake zargi sun musanta zargin da ake musu.

A gefe guda, wasu biyu daga ciki sun amsa laifinsu, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito cewa:

"Yayin da Kyari, sanye da shudin riga, da ‘yan sandan da ake tuhuma tare dashi, suka ki amsa laifin da ake tuhumar su da shi, wadanda ake tuhuma na 6 da na 7, Umeibe da Ezenwanne, sun amsa laifin da aka karanta musu a gaban kotun mai shari’a Emeka Nwite."

Da yake tabbatar da laifin da ya aikata, Umeibe ya kuma roki mai shari'a da ya tausaya masa, inji jaridar The Nation.



Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN