Abokan harkallar Abba Kyari 2 sun amsa laifin da ake tuhumarsu dashi
Bayan kawo Abba Kyari da abokan harkallarsa shida gaban kotu da safiyar yau Litinin, an bijiro da tuhume-tuhume da ake yi musu, sai dai, Abba Kyari da wasu mutum hudu da ake zargi sun musanta zargin da ake musu.
A gefe guda, wasu biyu daga ciki sun amsa laifinsu, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito cewa:
"Yayin da Kyari, sanye da shudin riga, da ‘yan sandan da ake tuhuma tare dashi, suka ki amsa laifin da ake tuhumar su da shi, wadanda ake tuhuma na 6 da na 7, Umeibe da Ezenwanne, sun amsa laifin da aka karanta musu a gaban kotun mai shari’a Emeka Nwite."
Da yake tabbatar da laifin da ya aikata, Umeibe ya kuma roki mai shari'a da ya tausaya masa, inji jaridar The Nation.
Legit