Yadda guragu suka sami lafiyar dole suka ruga da gudu kan kafafunsu bayan Jami'ai sun yi kokarin kamasu da mabarata, duba ka gani


Wani abun ban dariya da mamaki ya auku bayan wasu guragu da suka dade suna bara sun tashi suka ruga da gudu bayan Jami'ai sun yi kokarin kamasu a garin Thika da ke kasar Kenya. Shafin Jaridar isyaku.com ya samo.

38 daga cikin guragu da aka yi kokarin kamawa sun gudu da kafafunsu, wasu har sun fi Jami'ai gudu, domin dai sun kasa kamuwa bayan sun bude da gudu domin kaucewa kamasu.

Hukumomi na kokarin tsabtace garin ne sakamakon yadda mabarata suka cika muhimman hanyoyi kuma suna damun mutane da barace-barace.

Wani abin mamaki shi ne yadda wata mata wacce take rarrafe a kasa tana bara lokaci mai tsawo, ta mike ta ruga da gudu babu ko waiwaye domin kauce ea kamata.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN