Rikicin jam'iyar APC: Shugaba Buhari ya yi roko na musamman ga manbobin jam'iyar, duba abin da ya ce


Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya yi tsokaci kan rikicin shugabanci da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.

A wata sanarwa da kakakinsa, Malam Garba Shehu, ya fitar a Facebook, shugaba Buhari ya gargaÉ—i jagororin APC da su guji kiran suna da cin dudduniyar junansu.

Shugaban ƙasa ya kuma jaddada cewa babban ganganmin jam'iyyar APC na ƙasa na nan daram ranar da aka tsara 26 ga watan Maris 2022.

Haka nan Buhari ya roki mambobin APC da su kawar da duk wani saɓani dake tsakanin su, kuma su haɗa kai matukar suna son jam'iyyar ta cigaba da samun nasara a dukkan matakai.

A sanarwan an jiyo shugaba Buhari na kira ga mambobin APC kan, "Su duba babbar jam'iyyar hamayya PDP yadda ta koyi darasi daga rashin haÉ—in kai, rashin jagoranci da cin hanci."

Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN