Rikici ya kaure tsakanin sojoji da wasu matasa, an hallaka mutane akalla 6


Rahoto daga jaridar Daily Trust ya ce, an kashe mutane hudu a yankin Obayantor da ke karamar hukumar Ikpoba Okha ta jihar Edo bayan wani rikici da ya barke tsakanin wasu matasa da jami’an sojojin Najeriya.


An tattaro cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’ar da ta gabata a cikin yankin da aka ce suna ganin rigingimun shugabanci bayan tsige shugabansu na matasa (Okhaegele) tare da nada wani sabo.

Wani mazaunin garin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya yi zargin cewa wani ne ya dauki hayar sojoji ga al’umma da nufin kwato Okhaegele, kuma a lokacin fasinja an kashe sojoji biyu. Ya ce daga baya sojojin suka kaddamar da harin ramuwar gayya ga al’umma.

Wata majiya daga yankin ta ce sojojin sun zo da yawa inda suka rika harbe-harbe a sama, lamarin da ya tilastawa mutanen tserewa domin tsira da rayukansu. Ya ce an harbe mutane hudu har lahira.

Sai dai mai magana da yawun hedkwatar brigade 4 na rundunar sojin Najeriya, Benin, Yemi Sokoya, ya musanta cewa an yi hayan sojoji zuwa yankin.

Ya kuma yi watsi da labarin kashe sojoji biyu.

A cewarsa:

“Ba a yi hayan sojoji aiki ga al’ummar ba kuma ba a kashe wani soja ba. Ba harin ramuwar gayya ba ne, farmakin an yi shi ne bisa bayanan sirri na tara makamai."

Ya ce sojojin sun kwato wasu bindigogi guda uku, bindigogi kiran AK 47 guda biyu, wata nau'in bindigar guda daya, harsashi 32 da wayoyi.

Sai dai, wani rahoton jaridar Vanguard ya shaida cewa, shida ne aka kashe tare da wni soja daya.

Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN