Duba abin da ya faru da mutanen Shugaban kasa a taron jam'iyar APC na kasa

Ina mutanen Shugaban kasa?


Wata majiya ta bayyana cewa Abdullahi Adamu ne kadai ya sha a cikin ‘yan takarar da ake tunanin shugaban kasa Muhammadu Buhari yana marawa baya.

Idan aka tafi a haka kuwa, alamu na nuna Sanata Ken Nnamani da Hon. Farouk Adamu Aliyu ba za su zama mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa ba.

A jerin, babu sunan Ife Oyedele wanda ake tunanin yana da goyon bayan fadar shugaban kasa. A baya an ji cewa Oyedele ya dade yana tare da Buhari a siyasa.

Irinsu Salihu Lukman da Victor Gaidom sun shiga cikin jerin a matsayin shugabanni na kananun shiyyoyi yayin da aka nemi sunan Ismail Ahmed aka rasa.

Betta Edu da ake tunanin an yi waje da ita, za ta iya zama shugabar mata ta APC, sannan kuma kan gwamnonin APC bai hadu a kan Ismail Buba Ahmed ba.

Jerin da aka fitar

Ragowar wadanda aka fitar da sunansu kamar yadda TVC suka rahoto sun hada da:

Festus Fuanter

Muhazu Bawa Rijau

Dr. Ijeoma Arodiogbu

D. I kekemeke

Ahmed El-Marzuk

Uguru Mathew Ofoke

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN