Ina mutanen Shugaban kasa?
Wata majiya ta bayyana cewa Abdullahi Adamu ne kadai ya sha a cikin ‘yan takarar da ake tunanin shugaban kasa Muhammadu Buhari yana marawa baya.
Idan aka tafi a haka kuwa, alamu na nuna Sanata Ken Nnamani da Hon. Farouk Adamu Aliyu ba za su zama mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa ba.
A jerin, babu sunan Ife Oyedele wanda ake tunanin yana da goyon bayan fadar shugaban kasa. A baya an ji cewa Oyedele ya dade yana tare da Buhari a siyasa.
Irinsu Salihu Lukman da Victor Gaidom sun shiga cikin jerin a matsayin shugabanni na kananun shiyyoyi yayin da aka nemi sunan Ismail Ahmed aka rasa.
Betta Edu da ake tunanin an yi waje da ita, za ta iya zama shugabar mata ta APC, sannan kuma kan gwamnonin APC bai hadu a kan Ismail Buba Ahmed ba.
Jerin da aka fitar
Ragowar wadanda aka fitar da sunansu kamar yadda TVC suka rahoto sun hada da:
Festus Fuanter
Muhazu Bawa Rijau
Dr. Ijeoma Arodiogbu
D. I kekemeke
Ahmed El-Marzuk
Uguru Mathew Ofoke
Rubuta ra ayin ka