Kebbi: Dan NYSC ya yanke jiki ya fadi ya mutu a garin Dakin Gari yayin da yake kallon gasar kwallon kafa, duba yadda ta faru (Hotuna)


Wani dan yi wa kasa hidima NUSC mai suna Musa Momoh Tunde mai lambar aikin yi wa kasa hidima (KB/22A /2278 ya rasu yayin da yake kallon kwallon kafa a sansanin masu yi wa kasa hidima a garin Dakin Gari a jihar Kebbi.

Tunde ya karanci Public Administration a Federal polytechnic Bida, ya yanke jiki ya fadi ya mutu ranar Juma'a 26 ga watan Maris 2022 yayin da yake kallon gasar kwallon kafa da ake bugawa a cikin sansanin.

Darakta janar na NYSC na kasa Major-General Shuaibu Ibrahim ya aike sakon ta'aziyya ga iyalin Tunde.

An bizine Tunde a babbar Makabartar jihar Kebbi da ke garin Birnin kebbi.



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN