Kebbi: An kama mahaifi dan shekara 40 ya yi wa diyarshi mai shekara 13 fyade, duba yadda ta faru


Rundunar NSCDC reshen jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Aminu Bello bisa zargin yi wa diyarshi yar shekara 13 mai suna Hafsat fyade. Jaridar isyaku.com ya samo.

Rahotanni sun ce wani mutum ne ya rada wa jami'an bayan ya yi zargin abin da ke faruwa.

Kakakin rundunar na jihar Kebbi DSC Akeema Babatunde Adeyemi, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai.

Ya ce za su gurfanar da wanda aka kama a gaban Kotu da zarar sun kammala bincike.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN