Buhari ya nemi a soke wani sashe na sabuwar dokar zabe, duba ka gani


Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Talata, 1 ga watan Maris, ya bukaci majalisar dokokin kasar nan da ta yi wa sabuwar dokar zabe ta 2022 da aka sanya wa hannu kwaskwarima.

A wata wasika daga fadar shugaban kasa da shugaban majalisar dattijai, Ahmad Lawan ya karanta yau Talata, shugaba Buhari ya shaidawa majalisar dokokin kasar da ta duba batun cire sashe na 84 (12) gaba daya.

Wannan bangare na dokar zabe ya tanadi doka kan masu rike da mukaman siyasa da su yi murabus daga ofishinsu kafin su yi takarar fidda gwani a jam’iyyunsu na siyasa, inji rahoton Punch.

A cewar shugaban, tanadin dokar ta sashe na 84 (12 ) ta saba wa hakkin wadanda ke rike da madafun iko.

Karin bayani na nan tafe...

Source: Legit.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN