Alkalin Kotun Musulunci ya jefa magidanci Kurkuku sakamakon aikata halin bera kiri-kiri




Wata kotun shari’ar Musulunci a jihar Kano ta bayar da umarnin tsare wani mutum mai suna Yusha’u Ado mai shekaru 37 a gidan gyaran hali bisa samunsa da laifin satar kwalayen Maggi da aka yi.

Wanda ake tuhumar mazaunin Goron Dutse Quarters Kano, yana fuskantar tuhuma guda biyu da suka hada da zamba cikin aminci da damfara, Daily Trust ta ruwaito.

Tun da farko, dan sanda mai shigar da kara, Sifeta Abdullahi Wada, ya shaida wa kotun cewa wanda ya shigar da karar, Jamilu Ibrahim na Galandanci Quarters, ya kai kara ofishin ‘yan sanda na Sabon Gari a ranar 10 ga watan Maris.

Sifeta Wada ya ce wanda ya shigar da karar ya bayyana cewa, ya bai wa Ado kwalaye 260 na kayan dandano, wato Maggi da ya ajiye masa a shagonsa, kuma a lokacin da ya je daukar kayansa ya gano cewa kwalayen Maggin guda 22 da kudinsu ya kai N216,000 sun yi batan dabo.

Wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, Daily Trust ta ruwaito.

Alkalin kotun, Dakta Bello Khalid, ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake kara sannan ya dage sauraron karar zuwa ranar 8 ga watan Afrilu.

Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN