Yadda Jikan Sardauna Magajin Garin Sokoto ya rasu, duba abin da ya faru


Magajin Garin Sokoto, Alhaji Hassan Danbaba, Shugaban masu nada sarki na masarautar Sokoto, ya riga mu gidan gaskiya.

Danbaba, ya yanke jiki ya fadi ne a otel dinsa a Kaduna misalin karfe 11.30 na safe. Ya rasu a hanyarsa ta zuwa asibiti a Kaduna, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Daily Trust ta rahoto cewa wani na kusa da iyalansa, Alhaji Buhari Sarkin Tudun Jabo, ya tabbatar da Danbaba ya rasu a Kaduna bayan gajeruwar rashin lafiya.

Ya shaida wa Daily Trust cewa:

"Muna cikin kaduwa, don haka ba zan iya baka cikakken bayani ba a yanzu. Muna shirin kai gawar mamacin ne zuwa Sokoto inda za a masa jana'iza.

"Za a birne shi a garinsu a Sokoto a yau. Wannan babban rashi ne ba kawai ga iyalansa da Jihar Sokoto ba, amma rashi ne ga kasa baki daya."

Yadda Magajin Garin Sokoto ya rasu

Wata majiyar daban ta ce:

"Magajin ya zo Kaduna ne ranar Alhamis domin ya jajantawa Ministan Tsaro, Janar Aliyu Gusau, bisa rasuwar dan uwansa.

"Kamar yadda ya saba, ya sauka a otel dinsa, Stonehedge a birnin Kaduna.

"Gusau da Magajin sun yi shirin su bar Kaduna tare su tafi Abuja a ranar Asabar. Bayan ya yi wanka misalin karfe 11 na safe. Ya saka kaya domin ya tafi wurin Janar Gusau a gidansa.

"Muna shirin tafiya, ya yanke jiki ya fadi. Hadimansa suka taru suka dauke shi suka kama hanyar asibiti nan take. Amma, a hanya sai ya ce ga garinku."

Magajin Garin na cikin manyan yan Najeriya da suka hadu a Legas a makon da ta gabata domin tattaunawa kan yadda za a kawo karshen matsalolin Najeriya gabanin 2023.

Kafin rasuwarsa, Magajin Garin shine Direktan Jaridar THISDAY.

A dakaci karin bayani ...

Source: Legit.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN