Tap di jan: Wani matashi ya shake mahaifiyarsa har Lahira, duba dalili


A jiya Laraba, hukumar yan sanda reshen jihar Gombe ta jera wasu mutum takwas da ta kama da laifi daban-daban a faÉ—in jihar.

Jaridar The Nation ta rahoto cewa É—aya daga cikinsu, Garba Abubakar, ya shiga hannu ne bisa zargin shakare mahaifiyarsa, Salamatu Abubakar, yar shekara 45.

Kwamishinan yan sandan jihar Gombe, Ishola Babaita, ya ce wanda ake zargin ya yi wa mahaifiyarsa haka ne saboda ta masa faÉ—a ya daina shan miyagun kwayoyi.

Kwamishina ya ce:

"Wanda ake zargi ya shake mahaifiyarsa ne saboda ta masa faÉ—a ya dena ta'amali da miyagun kwayoyi. An yi gaggawar kai matar babban Asibitin Kumo, amma likita ya tabbatar da rai ya yi halinsa."

"Ina shawartar iyaye su maida hankali da sa ido wajen kula da 'ya'yan su kuma su tabbatar ba su faÉ—a muguwar É—abi'ar shan miyagun kwayoyi ba."

"Babban abun takaici wannan matar ta rasa rayuwarta a hannun É—an da ta tsugunna ta haifa, É—aya ne daga cikin sharrin kwayoyi."

Source: Legit.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN