Da duminsa: Yan fashi sun farmaki Bankuna 5 sun kashe yansanda da jama'a (Bidiyo)


Yan fashi da makami sun farmaki Bankuna da dama a garin Uromi da ke jihar Edo suka kashe mutane da dama da yammacin ranar Alhamis 24 ga watan Fabrairu, 2022. Shafin isyaku.com ya samo
.

Ganau sun ce Yan fashin sun farmaki Bankuna guda 5 lokacin hari da aka gudanar cikin tsari kamar yadda majiyar ta ce.

Fayafayin bidiyo da hotunan wajen da larin ya auku sun nuna gawakin mutane cikin jini kwance a kasa.

Ana fargaban cewa an kashe akalla yansanda biyu, mace guda daya da wani mutum a wannan farmaki a adadin farko da ake yadawa a labarin harin.

Sai dai kawo yanzu babu wani bayani daga jami'an tsaro a hukumance kan lamarin.

Latsa kasa ka kalli bidiyon farmakin

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=10221117244295847&id=1086336452

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN