Type Here to Get Search Results !

Da duminsa: Yan fashi sun farmaki Bankuna 5 sun kashe yansanda da jama'a (Bidiyo)


Yan fashi da makami sun farmaki Bankuna da dama a garin Uromi da ke jihar Edo suka kashe mutane da dama da yammacin ranar Alhamis 24 ga watan Fabrairu, 2022. Shafin isyaku.com ya samo
.

Ganau sun ce Yan fashin sun farmaki Bankuna guda 5 lokacin hari da aka gudanar cikin tsari kamar yadda majiyar ta ce.

Fayafayin bidiyo da hotunan wajen da larin ya auku sun nuna gawakin mutane cikin jini kwance a kasa.

Ana fargaban cewa an kashe akalla yansanda biyu, mace guda daya da wani mutum a wannan farmaki a adadin farko da ake yadawa a labarin harin.

Sai dai kawo yanzu babu wani bayani daga jami'an tsaro a hukumance kan lamarin.

Latsa kasa ka kalli bidiyon farmakin

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=10221117244295847&id=1086336452

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies