Da duminsa: Abba Kyari ya kamu da ciwon suga da hawan jini, Lauyansa ta bukaci Kotu ta bayar da belinsa


Mataimakin Kwamishinan yansanda Abba Kyari da ke fuskantar bincike a hannun hukumar NDLEA ya gaya wa Kotu cewa yana fama da cutar hawan jini da ciwon suga.

Kyari ya shaida wa Kotu haka ne a wani takardar neman beli da Lauyansa ta gabatar a gaban wani babban Kotun tarayya da ke Abuja.

Lauyan Kyari mai suna C.O Ikena, ta gabatar wa Kotun takardar mai lambar shari'a FHC/ANJ/CS/182/22, tana neman Kotu ta bayar da belin Abba Kyari bisa hurumin rashin lafiya.

Sai dai Alkalin Kotun mai suna Jasts Ekwo ya bukaci a gaya wa hukumar NDLEA wannan zance bayan Lauyan Kyari ya gaya wa Kotu cewa Kyari Yana hannun hukumar NDLEA a halin yanzu lokacin da Alkalin ya tambayi Lauyan Kyari cewa ina Kyari yake a halin yanzu.

Jastis Ekwo ya dage sauraron koken zuwa ranar 24 ga watan Aprilu domin ci gaba da sauraronsa. 

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN