Da duminsa: Abba Kyari ya kamu da ciwon suga da hawan jini, Lauyansa ta bukaci Kotu ta bayar da belinsa


Mataimakin Kwamishinan yansanda Abba Kyari da ke fuskantar bincike a hannun hukumar NDLEA ya gaya wa Kotu cewa yana fama da cutar hawan jini da ciwon suga.

Kyari ya shaida wa Kotu haka ne a wani takardar neman beli da Lauyansa ta gabatar a gaban wani babban Kotun tarayya da ke Abuja.

Lauyan Kyari mai suna C.O Ikena, ta gabatar wa Kotun takardar mai lambar shari'a FHC/ANJ/CS/182/22, tana neman Kotu ta bayar da belin Abba Kyari bisa hurumin rashin lafiya.

Sai dai Alkalin Kotun mai suna Jasts Ekwo ya bukaci a gaya wa hukumar NDLEA wannan zance bayan Lauyan Kyari ya gaya wa Kotu cewa Kyari Yana hannun hukumar NDLEA a halin yanzu lokacin da Alkalin ya tambayi Lauyan Kyari cewa ina Kyari yake a halin yanzu.

Jastis Ekwo ya dage sauraron koken zuwa ranar 24 ga watan Aprilu domin ci gaba da sauraronsa. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN