Duba abin da EFCC ta yi wa wani Sanata bayan ayyana son gadon kujerar Buhari


Hukumar EFCC ta gurfanar da sanata kuma tsohon gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha da zargin yashe kudaden gwamnati da suka kai N2.9bn.

An zarge shi da hada baki da wasu da suka hada da wani dan siyasan APC da wasu kamfanoni guda biyar a wannan wawura ta kudaden jama'a.

Takardun da Premium Times tace ta samo sun ce, hukumar ta EFCC ta shigar da kararraki 17 a ranar Litinin, a babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Baya ga sanata Okorocha, sauran wadanda ake tuhumar sun hada da Anyim Nyerere Chinenye, Naphtali International Limited, Perfect Finish Multi Projects Limited, Consolid Projects Consulting Limited, Pramif International Limited, da Legend World Concepts Limited.

An dai shigar da karar ne a daidai lokacin da sanata Okorocha ke bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2023.

Karin bayani na nan tafe...

Source: Legit.ng

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/G83TOEf1MUmDTiYaMTb02g

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakulabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN