Jami'an da suka yi wannan bajinta na aiki ne a yankin Dakwaro, a jihar MaraÉ—i, dake Jamhuriyar Nijar, kamar yadda Aminiya Hausa ta ruwaito.
Rahotanni sun bayyana cewa jami'an sun damke mutanen ne dumu-dumu, yayin da suke yunkurin safarar wasu makamai zuwa Najeriya.
Gwamnatin Maradi ta yaba wa jami'an
Bayan samun labarin abin da ya faru, gwamnan jihar Maradi, Shu’aibu Abubakar, ya garzaya yankin Dakwaro, inda aka kame mutanen, kuma ya jinjina wa jami'an bisa wannan nasara.
Gwamnan ya nuna jin daÉ—insa da kuma rokon jami'an tsaron su cigaba da kokarin dakile ayyukan irin waÉ—an nan mutanen.
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta daɗe da ɗaukar tsauraran matakan yaƙi da kuma kawo ƙarshen masu fasakwaurin makamai zuwa wasu ƙasashe, musamman waɗan da ke maƙwaftaka da Nijar.
Wane mataki gwamnatin Nijar ke É—auka?
Legit.ng Hausa ta gano cewa a baya-bayan nan sai da gwamnatin Nijar ta tsare wasu ma'aikatan ta bisa zargin hannu a wannan aika-aika ta safarar makami ba bisa ƙa'ida ba da kuma haramtattun kwayoyi.
A ɗaya bangaren kuma, gwamnatin Najeriya na ta faɗi tashin magance shigo da makamai ba bisa ƙa'ida ba daga wasu ƙasashe dake maƙwaftaka.
A halin yanzun, Najeriya na fama ayyukan ta'addancin yan bindiga a wasu jihohin arewa maso yamma.
Source: Legit.ng
Reported by ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye
https://chat.whatsapp.com/G83TOEf1MUmDTiYaMTb02g
Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN
Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN
Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN
Shafukan sada zumunta
Twitter twitter.com/isyakalabari
Facebook facebook.com/isyakalabari
RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI