Yara 3 sun yi wa mahaifinsu duka har ya mutu bisa zargin cewa ya sace masu wayar Android da suka saya


Wani mahaifi mai shekara 56 ya sha duka har ya mutu a hannun 'ya'yansa maza guda uku bayan sun yi zargin cewa ya sace masu wayar salula da suka hada kudi suka saya.

Lamarin ya faru ne a kauyen Shikangania da ke mazabar Lurambi , a gundumar Kakamega da ke kasar Kenya,

Yaran dai yan makarantar sakadari ne su biyu tare da wani kaninsu da ke ajin framare.

Rahotanni sun ce yaran sun gayyaci mahaifinsu ne zuwa wajen makoki da aka shirya bayan mutuwar makwabcinsu.

Sai dai yaran sun lallabi mahaifinsu zuwa wajen gari suka halaka shi a cikin daji.

Yan sanda sun kama yaran kuma ana gudanar da bincike.

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN