Daliba ta kone kurmus sakamakon gobara a dakin kwana na Jami'ar Taraba, duba yadda ta faru (Hotuna)


Wata dalibar aji daya a Jami’ar Jihar Taraba (TSU) ta mutu sakamakon gobarar da ta tashi a dakin kwanan daliban. 

A cewar gidan talabijin na Channels, dalibar mai suna Enuseh Lawi ta makale ne yayin gobarar a daren Juma’a. 

An tattaro cewa gobarar ta taba wasu sassa na Zenith Hostel da Enuseh ta ke zaune har ta mutu. 

An ce gobarar ta tashi ne yayin da dalibar ke kwance tana bacci, TheCable ta ruwaito. An ruwaito daga majiyoyin da ke da masaniya kan lamarin na cewa wasu dalibai mata suka balla dakin kafin a samu damar shiga. 

An ce an garzaya da ita asibitin kwararru na Jalingo inda aka ce ta rasu. Gobarar da ta shafi wasu sassa na dakin kwanan dalibai, ta jawo asarar dukiya da sauran kayayyaki masu daraja. 

A cewar majiyar: “An gaya mini cewa matar ta tafi karatu dare saboda jarrabawarta kuma ta dawo a gajiye, don haka ta yi barci. 

“Musabbabin wannan gobarar ta samo asali ne daga wani soket na wutan lantarki wanda ya kone kuma ba zato ba tsammani ya kama katifar da ke kusa da ita inda ta bazu ko’ina." 


Legit Hausa

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN