A ranar Juma'a ne aka zaɓi wata matashiya 'yar asalin Jihar Kano da ke arewacin Najeriya a matsayin wadda ta zo ta ɗaya a Gasar Sarauniyar kyau ta kasar.
Ga wasu daga cikin ƙayatattun hotunan matashiyar mai suna Shatu Garko.
Shatu Garko, mai shekara 18, ta doke zaratan mata 18 a bikin da aka gudanar ranar Juma'a da dare a Landmark Centre da ke birnin Legas.
Shatu ce mace ta farko mai hijabi da ta lashe gasar a tarihi kuma wannan ne karo na 44 na gasar wadda ake kira Miss Nigeria a Turance.
Nicole Ikot ce ta zo ta biyu, sai kuma Kasarachi Okoro da ta zo ta uku.
Ta karɓe kambun ne daga hannun Etsanyi Tukura 'yar Jihar Taraba, wadda ta lashe gasar a karo na 43 a 2019.
A cewar masu shirya gasar, wadda ta yi nasara za ta samu kyautar kuÉ—i naira miliyan 10, da zama a gidan alfarma na shekara É—aya, da sabuwar mota, da kuma zama jakadiya ta musamman ga wasu kamfanoni.
A shafinta na Instagram, matashiyar ta yi godiya ga waÉ—anda suka shirya gasar da kuma waÉ—anda suka É—auki nauyin wannan gasar.
Ta kuma gode wa jama'a bisa goyon baya da kuma soyayya da aka nuna mata
BBC Hausa
Reported by ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye
https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg
Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN
Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN
Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN
Shafukan sada zumunta
Twitter twitter.com/isyakalabari
Facebook facebook.com/isyakalabari
Rubuta ra ayin ka