Duba ababe 4 da kasurgumin dan bindiga Bello Turji ya nema a wasikarsa ta neman sulhu


Sanannen É—an bindigan nan da ya addabi wasu yankuna jihar Zamfara, Bello Turji, ya nemi a yi zaman sulhu domin kawo karshen kashe-kashe a yankunan jihar. 

A wasikar da ya aike wa shugaban Buhari, gwamna Matawalle, da Sarkin Shinkafi, Turji, ya sha alwashin aje makamansa bisa wasu sharuÉ—É—a da ya gindaya. 

A rahoton Aminiya Hausa ta samu kwafin wasikar mai shafi uku, É—auke da kwanan watan 14 ga watan Disamba. 

1. Gwamnati ta soke kungiyar yan sa'kai A cewarsa matukar gwamnati ta rushe Æ™ungiyar yan sa'kai to da izinin Allah duk wani kashe-kashe da yan bindiga ke yi ya zo Æ™arshe. Haka nan kuma yace dole sai an cire Æ™abilanci da ake nuna musu (wato fulani) a koma Æ™asa É—aya dunÆ™ulalliyar kamar yadda take a baya. 

2. Zaman sulhu da sarakuna da Malamai Ƙazalika a wasikar sa, Turji, ya nemi masarautar Shinkafi ta shirya musu zama da sarakunan Æ™asar nan da kuma manyan malamai domin tattaunawar adalci. Ya yi alÆ™awarin matukar aka shirya wannan zama, to zai karbi duk wata bindiga da ake aikata ta'addanci da ita ya miÆ™a wa hukumomin gwamnatin Najeriya. 

Wani É“angaren wasikar, yace: "Idan haka ta samu (Zaman Sulhu) to ni Muhammad Bello Turji Kachalla, na yi alÆ™awarin zan karbi dukkan bindigun da ake aikata ta'addanci da su na miÆ™a wa gwamnatin Najeriya." 

3. A daina hattarar mu a ko ina Sanannen É—an bindigan ya Æ™ara da tabbatarwa sarkin Shinkafi da gwamna Matawalle cewa su ba faÉ—a da gwamnati suke son yi ba, kuma ba wata Æ™ungiya suke yunkurin kafawa ba. Ya bayyana cewa cin zarafin da ake wa Fulani yan uwansu a faÉ—in Æ™asar nan da nuna musu bambanci shine ummul aba'isin wannan abubuwan na rashin zaman lafiya. 

4. Muna bukatar ganin Sheikh Gumi Abu na Æ™arshe kamar yadda ya rubuta a wasikarsa, Turji yace yayin zaman sulhu suna bukatar a haÉ—a manyan sarakuna da manyan malaman Æ™asar nan baki É—aya, kuma suna bukatar ganin Sheikh Ahmad Abubakar Gumi. Bugu da Æ™ari, yace sun san Sheikh Gumi, ya taba zuwa har inda suke ya musu waazi kuma wa'azinsa ya musu amfani, shiyasa suke son zaman lafiya. 

Daga Æ™arshe Turji yace wannan ne dalilinsa na rubuta wannan wasiÆ™a kuma dagaske yake ba da yaudara ba, kamar yadda baya son a yaudare su. 

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN