Da duminsa: Dan sanda ya yi marisa ya bindige matarsa da bindiga har Lahira ya fito daga gida ya buda wuta ya kashe wasu bayin Allah


An tabbatar da mutuwar mutane shida yayin da mutane biyu ke cikin wani mawuyacin hali a garin Kabete, da ke gundumar Nairobi a kasar Kenya. Shafin isyaku.com ya samo.

lamarin ya faru ne ranar Talata 7 ga watan Disamba bayan wani Dan sanda mai suna Constable Benson Imbasi, ya kashe matarsa bayan ya harbe ta da bindiga a wuya, daga bisani ya fito daga cikin gidansa ya fara harbin bayin Allah ba gaira ba dalili nan take ya kashe mutum biyar. Daga bisani ya juya bindiga ya harbe kanshi har Lahira.

Wata Takarda dangane da lamarin da ta fito daga shugaban sashe, kuma Daraktan Criminal Investigations, DCI, ya ce Dan sandan ya yi marisa kawai ya fara harbi da bindiga kirar AK47 ya kashe wasu samari uku nan take, kuma ya kashe wani dan acaba da ake kiransu matukan Boda-boda a kasuwar N a birnin Kabete.

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN