Hatsabibin dillalin miyagun kwayoyi da ya addabi jama'a a jihar Jigawa ya shiga hannu


Rundunar 'yan sandan Nigeria, a Jigawa ta yi nasarar kama wani mutum mai shekaru 48 da ake zargin hatsabibin dilalin miyagun kwayoyi ne. 

An kama shi ne a karamar hukumar Hadejia da ke jihar ta Jigawa kamar yadda ya zo a ruwayar The Nation. 

Jaridar The Nation ta rahoto cewa ASP Lawan Shiisu, mai magana da yawun rundunar yan sandan Jigawa, ne ya sanar da hakan a ranar Juma'a a Dutse, babban birnin jihar. 

Yadda aka kama wanda ake zargin Shiisu ya ce tawagar wasu 'yan sanda ne suka kama wanda ake zargin a ranar 15 ga watan Nuwamba misalin karfe 12.30 na rana. 

Ya yi bayanin cewa tawagar, yayin da suke sintiri a Hadejia sun kama wanda ake zargin a Gundun Sarki Quaters. 

Abin da aka kwace a hannunsa 

Kakakin yan sandan ya kara da cewa an samu kwallabe 43 na wasu abubuwa da ake zargin muggan kwayoyi ne a hannun wanda ake zargin.

 Ya ce za a gurfanar da shi a gaban kotu idan an kammala bincike. Shiisu ya kara da cewa an kama wasu mutane shida da ake zargin bata gari ne a karamar hukumar Kiyawa. 

Ya ce an kama su ne bayan kai samame a mabuyar bata gari da kauyen Balago a ranar 16 ga watan Nuwamba misalin karfe 7 na yamma. 

Da an kammala bincike suma za a gurfanar da su a kotu. 

Legit Nigeria

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN