Da duminsa: Dan Zuru ya Musulunta a babban Masallacin Juma'a na jihar Kebbi, duba dalili (Hotuna)



Wani dan Zuru mai suna Danjuma Danlami ya Musulunta a babban Masallacin Juma'a na jihar Kebbi ranar 5 ga watan Nuwamba, kuma ya amsa sunan Musulunci zuwa Muhammad Basharu.

Muhammad ya ce ya dade yana sha'awar shiga Musulunci, amma ya gamu da adawar haka daga iyayensa.

Ya ce yanzu iyayensa sun rasu sakamakon haka ya sami damar idar da sha'awa da aniyarsa ta shiga Addinin Musulunci.

Ya ce ya zo Birnin kebbi ne domin gudanar da aikin hannu a Unguwar Badariya kafin shigarsa Musulunci a yau.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN