Ana kashe mutane, Shugaba Buhari zai yi bayani gaban Allah inji Tsohon Gwamna, Bafarawa


Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya nemi shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dage a kan matsalar rashin tsaro.

Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa yace a halin yanzu yankin Arewa maso yamma yana cikin masifa. Bafarawa ya bayyana haka da BBC tayi hira da shi.

Babban ‘dan siyasar ya koka kan halin da mutanen yankin na sa da na shugaban kasa ke ciki. Jaridar Vanguard ta bibiyi hirar da aka yi da Bafarawa jiya.

“Sha’anin rashin tsaro wani bala’i ne da ya auko mana. Mutanen da ke can ne kurum za su iya bayanin halin da ake ciki a Sokoto da Zamfara.” – Bafarawa.

“Abin takaicin shi ne tsaron kasa na kan wuyan gwamnatin tarayya ne. Masu fadawa Buhari abubuwa suna tafiya daidai (ko suna ce masa da matsala ne?).”

“Idan suna fada masa abubuwa suna tafiya daidai ne, sun cuce sa, kuma sun cuce mu.”
Attahiru Dalhatu Bafarawa yake cewa Allah (SWT) ya san cewa ana cikin mummunan yanayi a yankinsa na Arewa maso yamma, domin mutane suna kuka.

Babu wanda ya isa ya shiga gonarsa - Bafarawa
“Yau, na je gida na dawo, na shaida da idanuna (ba fada mani aka yi ba). Mutane sun noma shinkafa da gero, amma ba za su iya kai amfaninsu gida ba.”

“Duk wanda ya je gona ya dauko kayan noman da ya samu, ba zai dawo da rai ba. A irinsu Zamfara, an tsare mutane, babu waya, kuma an rufe kasuwa.”
Da aka tambayi Bafarawa ko adawa ce ta sa shi yake irin wadannan maganganu, sai yace lamarin ya shafi har shugaban kasa, kuma Allah (SWT) zai tambaye shi.

Ana garkuwa da mutane a Arewa
Ko a farkon makon nan, kun ji cewa miyagun 'yan bindiga sun yi garkuwa da wasu masallata a baya-bayan nan a karamar hukumar Mashegu da ke jihar Neja.

'Yan bindigan sun sake yin garkuwa da mutane biyu da suka tafi kai musu lemu da kayan abinci.

Meyasa suke son gwamnan ya nemi takara a 2023?

Da yake zantawa da manema labarai a madadin shugabannin jim kaɗan bayan taronsu, Saleh Mandung Zazzaga, yace gwamna Lalong zai ɗaga martabar ƙasar nan zuwa inda mutane basa tsammani.

A cewarsa sun yi wannan hasashen ne duba da nasarorin da ya samu na rikice-rikice da kuma yadda ya saita sabanin da ake samu na ƙabila ko addini a jihar Filato, kamar yadda Leadership ta ruwaito.

Ya ƙara da cewa duk da rikicin da ake samu nan da can, gwamnan bai yi ƙasa a guiwa ba wajen jawo kowane bangare a cikin gwamnatinsa.

Yace:

"Lalong ne yake jagorantar ƙungiyar gwamnonin Arewa, kuma mafi yawan mutanen wannan yanki da ma na waje na yaba wa da tsarin mulkinsa."

Lalong yana da kwarewar da Najeriya ke bukata
Zazzaga ya kara da cewa gwamna Lalong yana da duk wata kwarewar siyasa wajen ɗaukaka Najeriya zuwa babban matsayi da kuma ƙara dankon haɗin kai.

Daga ƙarshe yace sun kammala shirin mara wa takarar gwmanan baya a 2023 kuma ba da jimawa ba zasu kaddamar da ita, amma a yanzun suna tattaunawar neman shawara ne daga kowane sashin ƙasar nan.

Gwamnan Atiku Bagudu na jihar Kebbi ya sallami ciyamomi 21 da kuma kansiloli dake faɗin jiharsa.

A wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar ranar Alhamis, gwamnan ya gode wa ciyamomin bisa aikin da suka yi a jihar.

Source: Legit.ng

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN