Type Here to Get Search Results !

Yanzu yanzu: Tashin hankali yayinda rikici ya sake ballewa a Kaduna, mutum 30 sun hallaka


Ana tsoron akalla mutum 30 sun rasa rayukansu yayinda aka kona gidaje a kauyukan Madamai da Abun dake karamar hukumar Kachia a jihar Kaduna.

A cewar tsohon shugaban gamayyar matasan Kaura, Derek Christopher, yan bindigan sun dira garuruwan ne misalin karfe 5 na yammacin Lahadi suka bude musu wuta, rahoton Daily Trust.

A cewarsa:

"An garzaya da wasu asibiti don jinyarsu."

Legit tayi yunkurin tuntubar Kakakin hukumar yan sanda a jihar Kaduna, ASP Muhammad Jalige, amma bai daga wayarsa ba.

Legit Hausa

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies