Shirin N-Power: Gwamnati Ta Fara Biyan Bashi Ga Mutum 14,021


Ma’aikatar Harkokin JinÆ™ai, Agaji da Inganta Rayuwa ta Tarayya ta bayyana cewa a yanzu ta fara yin biyan Æ™arshe na bashin da ya rage ga masu cin moriyar shirin tallafi na N-Power kashi na ‘A’ da ‘B’ su 14,021.

Hakan ya biyo bayan kammala warware ‘yar mishkilar da aka samu a tsarin da ake amfani da shi wajen tattara bayanan biyan kuÉ—in.

Babban Sakataren ma’aikatar, Alhaji Bashir Nura AlÆ™ali, shi ne ya bayyana haka a cikin wata takarda ga manema labarai da ya saki a Abuja a madadin ministar ma’aikatar, wato Hajiya Sadiya Umar Farouq.

AlÆ™ali ya ce tun a cikin watan Maris 2020 ne asusun ajiya na masu cin moriyar shirin su 14,021 su ka samu matsala, inda tsarin biyan kuÉ—in na Gwamnatin Tarayya mai suna ‘Integrated Financial Management Information System’ (GIFMIS) ya dakatar da biyan nasu kuÉ—in saboda wasu dalilai daban-daban waÉ—anda su ka haÉ—a da:

1) mallakar asusun banki sama da É—aya na masu cin moriyar shirin, da kuma

2) karÉ“ar wasu kuÉ—in daban a asusun banki na masu cin moriyar shirin kamar su albashi da alawus-alawus daga ma’aikatu da cibiyoyin Gwamnatin Tarayya daban-daban, na aikin dindindin ko na wasu shirye-shiryen da su ka shiga.

Ya ce waÉ—annan hidindimun sun saÉ“a wa Æ™a’idojin shirin sa-kai na N-Power wanda ka iya jawo babban laifi da ma cin hanci da rashawa.

Babban Sakataren ya Æ™ara da cewa ma’aikatar ta yi wani bincike mai zurfi tare da haÉ—in gwiwar ma’aikatun gwamnati da su ka dace kuma zuwa yanzu an warware mishkilar da ta shafi asusun mutum 9,066 ‘yan sa-kai a shirin, kuma har an fara biyan su.

Ya ce, “Bisa ga wannan tantancewar, yanzu an soma biyan alawus É—in watanni biyar da waÉ—annan ‘yan sa kan ke bi, kowanne wata a kan jimillar N150,000.00. Alawus É—in sauran mutum 4,955 kuwa an riÆ™e su har zuwa lokacin da za a kammala binciken da ake yi.

“Idan an tabbatar mutum ya karya Æ™a’idojin yarjejeniyar da aka yi, to za a yi wa irin waÉ—annan masu karya Æ™a’idar hukuncin da ya kamata kamar yadda doka ta tanada.”

Haka kuma AlÆ™ali ya ce akasin surutun da ake yaÉ—awa a cikin jama’a, wannan tsari babbar manuniya ce ta irim Æ™oÆ™arin da ma’aikatar ke yi na ganin ta magance wannan matsala maras daÉ—i da aka samu ta hanya fisabilillahi domin tsare gaskiya tare da kauce wa sake aukuwar hakan a nan gaba.

Ya ce, “Kamar dai yadda ake ta faÉ—a, binciken da ma’aikatar ta yi shi ne ya fi dacewa da Æ™asar nan kuma babbar manufar sa ita ce a kafa ingantaccen Shirin Inganta Rayuwa na Ƙasa, wato ‘National Social Investment Programme’ (NSIP) tare da tabbatar da cewa ana gudanar da shi cikin aminci kamar yadda mai girma Shugaban Ƙasa ya Æ™udiri aniyar tabbatar da tsare gaskiya da amana a wajen aiwatar da shirin a kowane lokaci.”

AlÆ™ali ya ce ma’aikatar ba ta ji daÉ—in tsaikon da aka samu ba wajen kammala wannan tsarin, “to amma ta na tabbatar wa da jama’a cewa ba za ta iya yin watsi da tsare gaskiya da amana ba a dukkan ayyukan ta.”

Rahotun leadership Hausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN