Type Here to Get Search Results !

An damke wasu mata 3 da ke taimaka wa yan bindiga a gandun dajin jihar Katsina (Hotuna)


Rundunar yansandan jihar Katsina ta kama wasu mata uku da ke safarar man fetur ga yan bindiga a cikin gandun dajin jihar.

Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito cewa, Kakakin hukumar yansandan jihar Katsina SP Gambo Isah, ya gabatar da matan ga manema labarai ranar Alhamis 23 ga watan Satumba. Ya ce jami'an yansanda masu yawon sintiri ne suka kama su a hanyar Katsina zuwa garin Jibia.

Wadanda aka kama su ne Dija Umar, 50; Ummah Bello, 45; da Nusaiba Muhammad, 16, dukkansu suna zaune a rukunin gidajen Malali da ke karamar hukumar Katsina a jihar Katsina.



Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies