Yansanda sun kama wani dan Fulani da ya boye a gandun daji dauke da bindiga kirar AK47 a jihar kudu


Jami'an rundunar yansandan jihar Ogun sun cafke wani yaro makiyayi mai suna Muhammad dauke da bindiga kirar AK47 bayan ya boye a cikin gandun daji ranar Talata 10 ga watan Agusta.

Bayan babban jami'in dansanda DPO na ofishin Imeko ya sami labari cewa an gano wasu Fulani guda biyu dauke da bindiga kirar AK47 a gandun dajin CAC Oha a garin Iwoye Ketu da ke karamar hukumar Imeko Afon.

Nan take DPO tare da jami'an ofishinsa, da marawar yan banga, maharbada, sauran yan sa kai, suka fuskanci gandun dajin. Bayan yan awowi a na bincike ne sai aka kama Muhammad boye kuma yana rike da bindiga kirar AK47.

Kakakin hukumar yansandan jihara Ogun DSP Abimbola Oyeyemi, ya sanar wa manema labarai tabbacin kama Muhammad bafulace dauke da bindiga kirar AK47. Ya ce Kwamishinan yansandan jihar Ogun CP Edward Awolowo Ajogun, ya bayar da umarnin mayar da binciken Muhammad zuwa sashen bincike na SCIID domin gudanar da binciken kwakwaf.

Ya ce ana zargin cewa Muhammad yana daya daga cikin gungun yan bindiga da ke addabar yankin ta hanyar sace mutane domin karbar kudin fansa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN