Yan bindigan da suka sace malamai da ɗalibai a kwalejin fasahar noma da dabbobi dake Bakura, jihar Zamfara, sun nemi a basu miliyan N250m kuɗin fansa.
Da yake magana da Punch ta wayar salula, shugaban kwalejin, Alhaji Habibu Mainasara, yace barayin sun tuntuɓe shi ta wayar salula.
Yace yan bindiga sun nemi a ba su miliyan N250m kuɗin fansar mutum 20 dake hannun su a yanzun sannan su sako su.
Mainasara yace:
"Sun faɗa mun cewa sai an basu kudin da suka bukata kafin su sako ɗalibai da malaman da suka kwashe a makarantar da nake jagoranta."
Wa zai biya waɗannan makudan kuɗi?
Sai dai shugaban makarantar bai fayyace cewa iyalan waɗanda aka sace ne zasu biya waɗannan kuɗaɗen ko kuwa gwamnatin jihar Zamfara.
Da aka tuntubi kakakin rundunar yan sanda reshen jihar Zamfara, Muhammad Shehu, yace sam hukumar yan sanda bata san ɓarayin sun nemi kudin fansa ba.
Shehu yace:
"Bamu da masaniya game da bukatar yan bindigan na kuɗin fansa amma muna iyakar bakin kokarin mu wajen kubutar da gaba ɗaya waɗanda aka sace."
Rahotun Legit News