Wani faifen bidiyo da ke yawatawa a shafukan intanet, ya nuna yadda ake zargin wani mugum mai gadi ya kashe uban gidansa wanda ma'aikacin bankin UBA ne. Kuma ya bizine gawarsa a bayan ginin gidansa a harabar gidan da karfe 11 na dare.
A wannan faifenn bidiyo, an jiyo Muryar wani dansanda a cikin harshen Hausa yana tambayar mai gadi cewa "Me yayi maka? Baka ci amana ba? Ya dauke ka tamkar Dan uwa".
Kazalika maigadin ya ce " Ni kadai na saka shi (a cikin rami ya bizine) Na bizine shi ne da wando da yake kwance da shi".
Kalli bidiyo a kasa:
https://www.youtube.com/watch?v=PadJ94Wjt1w