Da duminsa: Yan bindigan sun sace Manajan SRRBDA na garin Dutsin-Ma a jihar Katsina


Yan bindigan sun sace Manajan Sokoto Rima River Basin Development Authority (SRRBDA), na yankin Dutsin-Ma, Labaran Muhammed Dandume cikin daren ranar Alhamis, OBSERVERS TIMES ta ruwaito.

Wata majiya a Dutsin-Ma ta ce mutanen sun dauke Manajan ne a gidansa da ke gidajen SRRBDA da misalin karfe 11:47 na dare ranar Alhamis. 

Duk da yake an sami mabanbantan bayanai kan Labarin yadda Yan bindigan suka sace Manajan a samame da Yan bindigan suka gudanar a kasa da minti 20.

Kakakin hukumar yansandan jihar Katsina SP Gambo Isah, ya ce Yana sane da faruwar lamarin. Sai dai ya ce a bashi lokaci domin tattara bayanai kafin ya yi bayani kan lamarin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN