Gwamnatin JIhar Oyo da ke kudancin Najeriya ta bai wa bokayen da ke jihar umarnin su ɗauki kowane irin mataki domin kawo ƙarshen matsalar tsaro a jihar.
Kwamishinan YaÉ—a Labarai Dr Wasiu Olatunbosun ne ya bayar da umarnin ga majalisar masu maganin gargajiya ta jihar a madadin Gwamna Seyi Makinde.
Ya tabbatar musu da cewa gwamnatin jihar za ta ba su dukkan goyon bayan da suke buƙata domin taimakawa wajen samo maganin matsalar.
Matsalar garkuwa da mutane don neman kuɗin fansa ta karaɗe kowane yanki na Najeriya, ciki har da yankin kudu maso yamma inda ƙabilar Yarabawa ke da rinjaye mai yawa.
Kazalika, yankin na fuskantar rikicin manoma da makiyaya ƙari a kan ƙungiyoyi masu fafutikar ɓallewa daga Najeriya da nufin kafa ƙasar Yarabawa ta Oduduwa.
Rahotun BBC
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari