Ya kashe budurwarsa mai juna biyu tare da Jariri, duba dalili da abin da ya faru


Jami'an rundunar yansandan jihar Bauchi sun kama wani matum dan shekara 34 mai suna Lamido Gunduma bisa zargin kashe budurwarsa mai juna biyu tare da Jaririnta a karamar hukumar Jama'are.

Kakakin hukumar yansandan jihar Bauchi ASP Ahmed Wakil ya shaida wa manema labarai ranar Juma'a 14 ga watan Mayu. Ya ce wanda aka kama ya hada baki tare da abokinsa domin su zubar da cikin gaba da Fatiha da ya dirka wa budurwarsa yar shekara 35 mai suna Jamila Sa'idu, amma sai Jamila ta mutu yayin kokarin zubar mata da cikin.

Ya ce bayan mahaifin Jamila mai suna Sa'idu Iliyasu ya kai kara wajen yansanda ranar 7 ga watan Mayu da karfe 12 na rana.

Yansanda sun gano gawar Jamila a magudanar ruwa tare da jinjirin da ta haifa a gidan saurayinta Lamido a Unguwar Yari-mani da ke garin Jama'are. Yansanda sun gurfanar da Lamido gaban Alkalin Kotu.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN