Da duminsa: FG ta yi sulhu tsakanin Kwadago da El-Rufa'i, an yi yarjejeniya


Gwamnatin jihar Kaduna da kungiyar kwadagon Najeriya NLC sun yi yarjejeniya kan shirin sallamar ma'aikata kimanin 7000 da gwamnatin El-Rufa'i ke shirin yi.

Tun ranar Litnin NLC ta fara zanga-zanga da yajin aiki kan abinda gwamnatin jihar tayi.

Gwamnatin tarayya a ranar Alhamis ta shirya zaman sulhu tsakanin bangarorin biyu a Abuja.

PT ta rahoto cewa daga cikin yarjejeniyar da sukayi shine gwamnatin Kaduna ta cigaba da muradinta amma ta bi dokokin kwadago na korar ma'aikata bisa sashe na 20 na dokar kwadago.

Hakazalika sun yarje cewa NLC ba zata cigaba da yajin aikin ba amma kuma kada gwamnatin jihar ta hukunta duk wani ma'aikacin gwamnatin jihar da ya shiga yajin aikin.

Zaku tuna cewa gwamnatin Kaduna ta sanar da sallamar malaman jinya da malaman jami'ar KASU da suka shiga yajin aikin. Wannan yarjejeniyar ta rusa wannan hukunci.

Bayan haka an kafa kwamitin mutum 10; mutum 6 daga bangaren gwamnatin Kaduna, 3 daga bangaren NLC, da kuma mutum 1 daga bangaren gwamnatin tarayya domin tattauna yadda za'a wanzar da yarejejeniyar.

Dukkan bangarorin biyu sun rattafa hannu kan wannan yarjejeniya.

Source: Legit.ng


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN