Fitattun ‘yan Najeriya wadanda ke daukar nauyin ta’addanci za su fuskanci tsarin shari’a nan ba da jimawa ba kasancewar gwamnatin tarayya ta kammala shirye-shiryen gurfanar da su.
Babban Atoni Janar na Tarayya, Abubakar Malami (SAN) ne ya bayyana wannan ci gaban a ranar Juma'a, 7 ga watan Mayu, jaridar Punch ta ruwaito.
Malami wanda bai bayyana sunayen wadanda ake zargin ba ko kuma yawan mutanen da abin ya shafa ba ya bayyana haka ne yayin da yake zantawa da manema labarai na Fadar Shugaban Kasa a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, in ji jaridar The Cable.
Ya ce:
“Wani lokacin can baya, akwai wasu hukunce-hukuncen da aka yanke wa‘ yan Najeriya da ake zargi da hannu a cikin ayyukan ta’addanci a Hadaddiyar Daular Larabawa.
“Ina mai farin cikin bayar da rahoton cewa an dade ana gudanar da bincike kuma ya kai wani mataki na ci gaba.
“Tashi daga binciken, akwai, tabbas, akwai dalilai masu ma'ana na zato cewa yawancin 'yan Najeriya, manyan mutane, hukumomi, da sauran su, suna da hannu a daukar nauyin ta'addanci kuma an gabatar dasu don gurfanar dasu.
“A zahiri, gaskiya ne cewa gwamnati tana tuhuma kuma hakika ta fara shirya matakai na gurfanar da wadannan manyan mutane da aka gano suna tallafawa ta'addanci. Gaskiya ne.”
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Ina bibiyar shafinka, yana matukar bani labarai masu inganci sosai, nima blogger anan arewa maso gabas din Nigeria, ga address din website dina https://www.netage.com.ng
ReplyDelete