Mazauna kauyen Majifa da 'yan banga a karamar hukumar Kankara sun kashe a kalla mutane 30 da ake zargin yan bindiga ne a jihar, Daily Trust ta ruwaito.
Duk da cewa bayyana basu kamalla fitowa ba a lokacin hada wannan rahoton, majiyar Legit.ng ta gano cewa yan kauyen sun kafa wa yan bindigan tarko ne.
Wani mazaunin kauyen ya shaidawa majiyar Legit.ng cewa lamarin ya faru ne da asubahin ranar Litinin.
"Mazauna kauyen sun samu labarin cewa yan bindigan na shirin kawo musu hari cikin dare, hakan yasa suka kafa musu tarko kuma Allah ya basu nasara suka fatattake su suka kashe a kalla 30 daga cikin yan bindigan," in ji shi.
Amma, ya ce wasu yan bindigan sun dawo a kan rakuma sun kwashe gawarwakin, inda ya ce, "Mutanen kauyen na jira gari ya waye kafin su kona gawarwarkin amma suka farka suka ga an kwashe gawarwakin, sannan wasu da ke kauyen da ke makwabtaka da su sun tabbatar wasu mutane sun kwashe gawarwakin a kan rakuma."
Wannan shine karo na uku a cikin makonni uku da mazauna kauyen ke yin fito na fito da yan bindigan.
A ranar Lahadi, mazauna garin Magama da karamar hukumar Jibia sun yi gaba da gaba da yan bindiga sun kashe uku daga cikinsu.
Amma, da aka tuntubi kakakin yan sandan jihar, SP Isah Gambo, bai iya tabbatar da afkuwar lamarin ba inda ya ce zai tuntubi DPO na kananan hukumomin.
Gambo ya ce rahoton kashe yan bindiga 30 din ba gaskiya bane domin a lokacin da DPO da tawagarsa suka tafi garin ba su tarar da koda gawa daya ba.
Source: Legit Nigeria
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Rubuta ra ayin ka