Sojoji sun kashe Abu Aisha da wasu manyan kwamandojin ISWAP 17 a Damasak


Dakarun Sojojin Nigeria sun kashe babban kwamandan ISWAP, Bukar Gana Fitchmeram (aka Abu A'isha) da wasu mayakansa da suka zo ramuwar gayya a Damasak amma suka haÉ—u da ajalinsu hannun sojoji a ranar Alhamis.

Rundunar Sojin ta ce ƴan ta'addan sun gamu da karshen su a yayin da suka kai hari bayan kashe manyan kwamandojin ISWAP 12 a ƙaramar hukumar Mobbar sakamakon hare-haren ƙasa da sama da sojojin suka shafe yi na kwanaki 7.

Kakakin soji, Birgediya Janar Mohammed Yerima, ne sanar da hakan ta shafin Twitter na rundunar a ranar Juma'a.

A baya an ruwaito cewa Æ´an ta'addan sun kashe wasu sojoji sun kuma lalata ginin Majalisar Dinkin Duniya yayin harin da suka kai Damasak amma Yerima, a ranar Juma'a ya ce an kashe manyan kwamandojin ISWAP da jiragen yaki yayin harin.

Ya yi wa sanarwar laÆ™abin 'Yadda manyan kwamandojin ISWAP suka gamu da Æ™arshen su yayin da suka dawo É—aukan fansa a Damasak.'

Sanarwar ta ce, "Hare-haren sama da aka kai a Tudun Wulgo, Zafi, da Tumbun Alhaji, Kusuma, Sigar a Ngala da Arijallamari a Abadam, Marte a Æ™aramar hukumar Ngala ya yi sanadin kashe manyan kwamandojin ISWAP.

"Kwamandojin da aka kashe yayin harin saman sun hada da Mohammad Fulloja, Ameer Mallam Bello, Ba'a kaka Tunkushe , Abu Muktar Al-Ansari, Ameer Abba Kaka, Abu Huzaifa, Ameer Modu Kwayem, yayin da Goni Mustapha wanda shine babban limamin ISWAP ya tsira da raunin harsashi."

Rundunar sojojin ta kara da cewa hare-haren sama da ƙasa da aka kai a ranar 6 ga watan Afrilu ya yi sanadin mutuwar manyan kwamandojin ISWAP biyu ciki har da Abu-Rabi da Muhammed Likita da masu tsaronsu a kusa da Kusuma, Sigir a ƙananan hukumomin Ngala da Arijallamari, Abadam.

An kuma lalata wuraren da Æ´an ta'addan ke ajiye makamansu yayin samamen da dakarun Operation Lafiya Dole suka kai.

A daren ranar 10 ga watan Afrilu, Yerima ya yi bayanin cewa dakarun Sojojin sun ritsa wasu kwamandojin yan ta'addan uku a kusa da Wulgo/Logomani kusa da iyakar Kamaru yayin da suke kokarin satar shanun mutanen yakin, wadanda aka kashe sune Ameer Umar, Abu Ubaida da Abu Salim.

A cewarsa, wannan illar da aka yi wa Æ´an ta'addan ya saka sun fara kai hare-hare suna satar abinci da magunguna don kulawa da yan uwansu da suka jikkata.

Har wa yau, rundunar sojin ta ce a ranar 11 ga watan Afrilu, sojojin sun halaka wasu Æ´an ta'addan a cikin motocci masu bindiga 5 a Damasak.

Ya ce an wasu daga cikin Æ´an ta'ddan sun samu shiga garin na Damasak inda suka kone gine-gine suka sace kaya kafin suka tsere.

Wannan ba shine karo na farko da aka kai hari Damasak ba amma duk da hakan sojojin na cike da izza a yakin da suke yi da Æ´an ta'addan duk da akwai Æ´an leken asiri da ke sanar da Æ´an ta'addan inda sojojin suke.

Source: Legit Newspapers


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN