Uwargida ta banka wa Amarya wuta ta mutu mako 7 bayan aure a jihar Niger, duba yadda ta faru


Wata uwargida ta kashe Amaryar mijinta mai suna Fatima yar asalin jihar Katsina bayan ta banka mata wuta har ta mutu.


Lamarin ya faru ne ranar Talata 23 ga watan Maris kimanin makonni bakwai bayan aurensu da mijinta dan jihar Niger.


Wani dan uwan Amaryar ya gaya wa Katsina post cewa Uwargida da Amarya basu zaune a gida daya. 


Sai dai Uwargida ta yi tattaki har gidan da Amarya take zaune kasancewa babu nisa daga gidan da take, ta yi mata dan karen duka har ta galabaita, daga bisani ta kulle ta a cikin daki kuma ta banka wa gidan wuta har Amarya ta kone ta mutu a cikin gobarar.


Za a yi janaizan Amarya a gidansu da ke Sabuwar Unguwa a cikin birnin Katsina ranar Laraba 24 ga watan Maris.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN