Hotuna: Yansanda sun damke Uwargida da ta kashe Amarya da tabarya ta kone gawarta


Rundunar yansandan jihar Niger ta kama wata mata yar shekara 24 mai suna Amina Aliyu bisa zargin kashe Amarya da mijinta ya auro a jihar Niger.

Shafin ISYAKU.COM ya ruwaito cewa an kashe Amarya mai suna Amina Aliyu ranar Talata 23 ga watan Maris, inda aka sami gawarta kwance a gidanta kuma rabin jikinta a kone da wuta. An yi zargin cewa an yi amfani da tabarya ne aka kasheta.


Kakakin yansandan jihar Niger DSP Wasiu Abiodun ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

A wata takarda da Abiodun ya sa wa hannu amadadin Kwamishinan yansandan jihar Niger, ya ce :

 


"Ranar Talata wani mutum mai suna Bello Lawal da ke Gwari Motors Bosso road Minna, ya kawo Kara amadadin Alhaji Aliyu Abdullahi mai shekara 45 da ke zaune a Mandela road Sauka Kahuta,  cewa an sami gawar matarsa kuma Amaryarsa mai suna Fati Aliyu jina jina, jikinta kuma a kone da wuta.

"Bayan samun wannan koke ne yansanda suka shiga aiki, kuma suka kama uwargidan mai suna Amina Aliyu yar shekara 24. Yansanda sun sami tabarya da ake zargin Amina ta yi amfani da shi ta kashe Fatima saboda yar uwar Amina ta shaida wa yansanda haka, kuma shaida ce domin a gaban jdonta lamarin ya faru.

Yansanda sun dauki tabarya da ake zargin Amina ta kashe Fatima da shi, kuma za mu gurfanar ta Ammina a gaban Kotu da zarar mun kammala bincike" Inji DSP Wasiu Abiodun.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN