Yansanda 4 sun yi mutuwar gaggawa a jihar kudu, duba abin da ya faru


Yan bindiga da ake zaton masu sace mutane ne, sun kashe yansanda guda hudu a wajen binciken ababen hawa na yansanda, a birnin Calabar a jihar Cross Rivers.

Mun samo cewa lamarin ya faru da sanyin safiyar ranar Alhamis 25 ga watan Fabrairu.

Mun kuma samo cewa Yan bindigan sun yi wa yansandan kwanton bauna ne a Ayanmbat da ke kusa da Idundu a unguwar Aka Efaka a Birnin Calabar.

An ce yansandan sun gamu da ajalinsu ne, yayin da suka je domin su kubutar da wasu da ake zargin an sace su domin a karbi kudin fansa.

Bayanai sun ce yansanda sun dukufa domin gano wadanda suka aikata wannan ta'asa 






Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN