7 daga cikin yan makarantar mata 317 da aka sace a Zamfara sun tsere sun dawo gida


Bakwai daga cikin yara mata yan makaranta guda 317 da aka sace a makarantar màta da ke Jangebe a jihar Zamfara sun gudu daga hannun wadanda suka sace su, Channels TV ta làbarta.

Ana zargin cewa yan bindiga ne suka sace su da sanyin safiyar ranar Juma'a 26 va watan Fabrairu.

Channels TV ta ce wani mazauni yankin da lamarin ya faru ya rada mata cewa hakika yaran guda 7 sun dawo gida da yammacin ranar Juma'a 26 ga watan Fabrairu.

Ya ce yaran sun sami sace jiki ne yayin da suke tafiya a cikin gandun daji kuma suka tsere..

Ya ce ana sa ran cewa akwai Karin wasu yaran da suka tsere kuma ana sa ran isowarsu gida.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN