Dattijo ya mutu lokacin da yan bindiga suka sace shi da yayansa mata guda 2 a jihar Katsina


Wani dattijo mai suna Hassan Bahago ya rasu sakamakon bugun zuciya bayan yan bindiga sun shiga gidansa suka sace yayansa mata guda biyu a rukunin gidaje na Shagari quarters a garin Funtua, da ke karamar hukumar Funtua a jihar Katsina.

Wannan mumunan lamari ya faru ne ranar Alhamis da dare.

Rahotanni sun ce dattijon, wanda daya ne daga cikin dattijan Mujami'ar ECWA ta Funtua, ya kamu da ciwon zuciya lokacin da Yan bindigan suke janye da shi tare da yayansa mata guda biyu, Saratu da Jennifer, sai ya yanke jiki ya fadi ya mutu nan take.

Yan bindigan sun sace wani ma'aikacin Bankin First Bank mai suna Mr Alex, kuma suka kashe shugaban yan Banga na garin Alhaji Ali Bahago lokacin da ya fito domin ya taimaka wajen dakile harin yan bindigan, amma ya rasa ransa sakamakon harbe harben bindiga tsakaninsa da yan bindigan.

Wani mazauni Shagari quarters mai suna Sagir Muhammed, ya shaida wa Jaridar Thisday cewa yan bindigan sun kai hari a rukunin gidajen da misalin karfe 11:15 na dare, suka tafka ta'asa, suka raunata mutane da dama, kuma sun dauki fiye da minti 30 suna 


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN