Wani dan sanda a kasar Zimbabwe ya kashe wani jariri mai wata 9 da haihuwa lokacin da ya je dukan mahaifiyarsa da Kulkin yan sanda amma sai ya kwade Jaririn da yake goye a bayan mahaifiyarsa sakamakon haka ya mutu nan take.
Wannan lamari ya faru ranar Litinin, kafin Gwamnati ta sa dokar hana fita sakamakon COVID-19.
Wani faifen bidiyo da ke yawatawa a shafukan intanet ya nuna yadda mahaifiyar yaron ta rike gawar Jaririn da hannu daya kuma ta damke dan sandan da hannu daya yayin da dan sandan ke kokarin kwace kansa.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari