Zuru Emirate Council ta karbi Bakuncin Kungiyar Bright Girls


Mai martaba sarkin Zuru, Major General Muhammadu Sani Sami na 2 ya bada shawarar cewa ya kamata matan Ciyamomi na yankin Zuru da Kuma kansiloli mata su hada kai da wannan Kungiya domin cigaba da ilmantar da sauran matan cikin gida akan muhimmancin tsabtar abinci domin samun ingantarciyar lafiya ga Al'umma. 
   

Shugaban Karamar hukuma na Zuru Hon Kabiru Turaki, ya raka kungiyar cikin Kasuwa  domin  fadakarwa akan muhimmancin kula da tsabta ga abubuwan da mu ke ci. 


A cikin garin fakai, kungiyar ta samu tarbo na musamman daga Sarkin Fakai Alh Hudu Dan Malam ACP retired. Ya Kuma yi alkawarin za su dauki dukkan matakin da ya dace akan kula da tsabtar abinci.
A wani bangaren, Sarkin Mahuta Alh Ibrahim Falke Anama, ya yi kira ga wasu masu sana'ar nama da su daina  dauko musai suna gyarawa domin Sayarwa. 


Shima shugaban karamar hukuma na Fakai, ya yabawa kungiyar game da wannan tunani.
 
A yankin Danko wasagu, Matar Chairman Hajiya Hussai Sulaiman Shindi, da kuma mataimakin Chairman, sun raka kungiyar zuwa Kasuwa domin fadakarwa da kuma bayarda tallafi.


Daga karshe, kungiyar ta shiga garin Sakaba ta Kuma Sami tarbo na musamman ga Chiefdom na Sakaba Muhammed Sakaba da kuma Ubankasa Mai Diri Alhaji Usman Mai Diri, inda ya  gayyato mata a majalisarsa sa domin karbar bayanai a kan tsabtar kula da kayan abinci.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN