Shehu Sani ya yi wa Buratai 'wankin babban bargo' a kan wa'adin da ya bai wa Boko Haram


Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani, a ranar Alhamis, ya caccaki shugaban rundunar sojin kasa, Lt. Janar Tukur Buratai, a kan yadda yace ta'addanci zai iya cigaba da wanzuwa har nan da shekaru 20 a Najeriya.

The Punch ta ruwaito yadda shugaban sojin kasa yayi wata magana bayan 'yan kwanaki da 'yan Boko Haram suka kashe manoman shinkafa 43 a jihar Borno 

Tsohon sanatan ya mayar da martani a kan maganar, ta shafinsa na kafar sada zumuntar zamani ta Twitter a ranar Alhamis, inda yace kalaman Buratai suna nuna karewar basira da rashin dabarun yaki.

Kamar yadda Shehu Sani ya wallafa, "Sanar da mutanenmu cewa tabarbarewar harkokin tsaro za su cigaba har na tsawon shekaru 20 alamace da ke nuna gazawa da karewar basirarka a matsayinka na soja. 

"Kuma alama ce wacce take nuna kana bukatar murabus, sannan kuma kana nuna wa duniya alamar cire rai daga samun nasara ne."

A cewarsa, ya zama tilas mutanen kirki, maza da mata, su hada karfi da karfe wurin kawo karshen rikicin addinin. Dr Gumi, wanda shine shugaban KHF ya fara shirin kawo karshen rikicin addini da ke addabar kudancin Kaduna, wanda yake hana cigaba da zaman lafiya.

Source: legit


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN