Maryam Sanda ta na shirin daukaka kara zuwa Kotun koli ta Najeriya bayan Kotun daukaka kara ta jaddada hukuncin Kotun tarayya na kisa ta hanyar ratayewa har ta mutu bayan Kotun ta same ta da laifin kashe mijinta Bilyamin Muhammed.
Ranar Juma'a 4 ga watan Disamba ne wata Kotun daukaka kara a birnin Abuja ta jaddada hukuncin kisa da Kotun tarayya ta yanke mata.
A shekata ta 2017, rikicin cikin gida ya kaure tsakanin Maryam da mijinta Bilyamin, inda ake zargin ta yin amfani da wuka ta caka masa a wurare da dama, lamari da ake zargin ya yi sanadin mutuwarsa.
Jim kadan bayan jaddada hukuncin a Kotu, Lauyan Maryam Sanda mai suna Joe Gadzama SAN, ta ce za su daukaka kara zuwa Kotun koli, Kotun daga ke sai Allah ya isa a Najeriya.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari