Rikici tsakanin wasu kunguyoyin asiri guda biyu ya yi sanadin kashe wata budurwa da saurayinta a cikin al'umman Oriuzor da ke karamar hukumar Ezza ta arewa a jihar Ebonyi ranar Lahadi 29 ga watan Nuwamba.
An kashe masoya Chinenye tare da saurayinta Chinedu Nwode sakamakon rikicin gaba tsakanin kungiyoyin asiri na Baggers da na Aye Confraternities.
An kashe masoyan ne lokacin da suke dawowa daga wajen wani bikin zanen suna da aka yi ma wani jariri a garin Oriuzor zuwa Onueke.
Kakaklin hukumar yansandan jihar DSP Loveth Odah, ta tabbatar da faruwar lamarin ranar Talata 2 ga watan Disamba.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari