Daliban jami'o'i a Najeriya ka iya sanin makomarsu a yau Talata yayin da kungiyar ASUU ta malaman jami'a ke tattaunawa da tawagar ma'aikatar kwadago dom kawo karshen yajin aiki.
Ministan Kwadago Chris Ngige ya ce tattaunawar tasu ta kai kashi 98 cikin 100 domin kawo karshen yajin aikin da malaman suka shafe fiye da wata takwas suna yi.
Mai magana da yawun ministan kwadagon, Charles Akpa, ya ce bangarorin biyu za su shaga tattaunawar a yammacin yau, wanda shi ne irinsa karo na takwas.
A zaman da suka yi a baya, gwamnati ta amince ta biya malaman alawus na naira biliyan 40 da kuma biliyan 30 na farfado da kayayyakin karatun jami'o'in.
Babban abin da ke jawo tsaiko a tattaunawar shi ne maganar albashin malaman da gwamnati ta ki biya na tsawon lokacin da suke yajin aikin, wanda suka ce sai an biya su sannan za su ci gaba da aiki.
Sai dai gwamnati ta bukaci su ci gaba da aikin kafin a biya su albashin.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari