Yanzu yanzu: Kotun Abuja ta bayar da belin yan zanga zangan EndSars kan N50,000 kowannensu


Wata Kotun Majistare a birnin Abuja, ranar 11 ga watan Nowamba, ta bayar da belin Paul Akinwumi, Davo Chom, Abdulsalam Suberu, Kabiru Gasali, Yaziru Bashiru da wataa yar Jarida da take daukan labarai a lokacin zanga zangar EndSars.

The Cable ta labarta cewa an garkame masu zanga zangan ne a Kurkuku bayan Alkalin Kotun ya ki amincewa da neman belin wadanda aka yi kara a gaban Kotun da Lauyansu Tope Akinyode ya gabatar.

Sai dai a zaman Kotun na ranar Laraba, Alkalin Kotun Abdulrazak Eneye, ya bayar da belinsu a kan Naira dubu hamsin kowannensu tare da wadanda zai tsaya wa kowannensu.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN